in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi Jinping ya jadadda bukatar a mayar da hankali kan aikin farfadowa a yankin kudu maso gabashin kasar da girgizar kasa ta shafa
2013-05-23 20:12:59 cri
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya bukaci gwamnatocin kananan hukomi a lardin Sichuan dake kudu maso yammacin kasar da mummunan girgizar kasa ta abkawa a watan da ya gabata, da su mayar da hankali kan aikin farfadowa.

Shugaba Xi ya bayyana hakan ne lokacin da ya ziyarci yankin Lushan da bala'in ya fi shafa, inda ya bukaci kananan hukumomi da su kimanta irin barnar da bala'in ya haddasa, kana su tsara wani shirin farfadowa a matakin kananan hukumomi.

Xi ya ce kamata ya yi shirin ya yi la'akari da tattalin arziki da yanayin yankin, tare da samar da dama ga yankunan da bala'in ya shafa ta yadda za a farfado tare da samun ci gaba.

Ya ce kamata ya yi gwamnatocin yankunan su fito da tsare-tsaren farfadowa da suka dace wadanda za su kai ga zuba jari, kudin shiga, cin gajiyar filaye, samar da aikin yi da kuma tsaron jama'a.

Idan ba a manta ba a ranar 20 ga watan Afrilu ne wata girgizar kasa mai karfin mako 7.0 ta abkawa yankin Lushan, inda mutane a kalla 196 suka mutu. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China