in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Philippines za ta sanar da rahoton bincike kan lamarin garkuwa da mutanen Hongkong a mako mai zuwa
2010-09-18 20:39:17 cri
A ranar 17 ga wata, Gwamnan hukumar yankin musamman na Hong Kong na kasar Sin, Donald Tsang ya bayyana cewa, yanzu bangaren 'yan sanda na Hongkong yana kokarin tattara dukkan shaidu game da lamarin garkuwa da wasu mutanen Hongkong da ya faru a kasar Philippines, amma har zuwa yanzu ba a samu rahoton da kwamitin binciken lamarin na kasar Philippines ya gabatar ba.

Dadin dadawa a yau ranar 18 ga wata, mashawarcin shugaban kasar Philippines a fannin sadarwa da tsare tsaren cikin gida, Ricky Carandang ya bayyana cewa, kasar Philippines za ta gabatar da kwafin rahoton bincike ga hukumar kasar Sin a ranar 18 ko 20 ga wata, kuma za ta sanar da abubuwan dake cikin wannan rahoton bincike ga jama'ar kasar Philippines a farkon mako mai zuwa. (BIlkisu)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China