in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar yaki da ta'addanci ta MDD ya mai da hankali kan Mali, yankin Sahel da Somaliya
2013-05-11 16:48:37 cri
Hukumar yaki da ta'addanci ta MDD, wadda ke sa ido kan harkokin kungiyar Al-Qaida na kara himma da hadin gwiwa da sauran hukumomin MDD dake da alaka da hakan, domin a samu shawo kan sabuwar barazanar kungiyar dake kunno kai a kasar Mali, yankin Sahel da kuma kasar Somaliya, in ji shugaban hukumar yayin da yake jawabi ga kwamitin sulhu na MDD a ranar Jumma'a.

A cikin jawabinsa ga hukumomin yaki da ta'addanci da hana yaduwar makaman kare dangi da ke karkashin shugabancin kwamitin sulhu, shugaban kwamitin da aka kafa bisa kuduri na 1267 a shekarar 1999, da kuma na 1989 na shekarar 2011 kan kungiyar Al-Qaida, Gary Quinlan ya ce, ya dace a yi dukkan kokarin tabbatar da cewa, takunkumin da aka kafa ya yi amfani sosai wajen hana kungiyar al-Qaida da mukarrabanta yin barazana ga zaman lafiya da tsaro a duniya.

Matakan sun kunshi tabbatar da cewa, ana kara sabunta takunkumi kan kungiyar al-Qaida, kuma su zamo da inganci don a samu aiwatar da su.

Dangane kuma da batun kasar Mali da yankin Sahel, kwamitin ya dora takunkumi kan dukkan kungiyoyin dake da alaka da kungiyar al-Qaida, gami da shugabanninsu da ma sauran jama'ar dake da nasaba da su.

A kuma ranar Jumma'a har ila yau, kwamitin sulhu ya saurari rahoto daga shugaban kwamitin yaki da ta'addanci Mohammed Loulichki, inda ya bayyana cewa, za a yi wani taro na musamman da zai mai da hankali a kan kara bunkasa hadin gwiwa da ba da tallafi ga kasashen yankin Sahel domin a karfafa matsayinsu kan yaki da ta'addanci. (Lami Ali)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China