in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Sin ya jaddada inganta haduwar moriyar Sin da Faransa
2013-04-26 19:30:19 cri
Ranar 26 ga wata, Li Keqiang, firaministan kasar Sin ya gana da François Hollande, shugaban kasar Faransa da ke ziyara a nan birnin Beijing, hedkwatar kasar Sin, inda ya nuna cewa, Sin da Faransa na taimakawa juna sosai a fannin raya tattalin arziki, don haka akwai babbar dama wajen yin hadin gwiwa a tsakaninsu. Ya zama dole su inganta samun moriyar juna, da sabunta hanyoyin yin hadin gwiwa, a kokarin kara samun sakamako mai kyau.

Har wa yau kuma, a yayin ganawar, Li Keqiang ya ki yarda kan ba da kariyar cinikayya ta hanyoyi daban daban, kana ya jaddada muhimmancin habaka fannonin yin hadin gwiwa a tsakanin Sin da Faransa. A cewarsa kuma, kasar Sin za ta ci gaba da mara wa kasashen Turai baya wajen tinkarar matsalar bashi da ke addabarsu.

A nasa bangaren kuma, François Hollande ya ce, ya kamata kasashen 2 su himmantu wajen tafiyar da harkokin duniya yadda ya kamata da tinkarar kalubale iri daban daban. Kasar Faransa tana son zurfafa da habaka hadin gwiwar da ke tsakaninta da Sin a fannoni daban daban, da kin yarda da ba da kariya kan harkokin cinikayya tare, a kokarin samun moriyar juna da nasara tare. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China