in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU na nazarin hanyoyin kawar da yunwa a nahiyar Afrika
2013-05-08 10:30:57 cri

Kungiyar tarayyar kasashen Afrika (AU), kungiyar cimaka da noma ta majalisar dunkin duniya (FAO) sun gudanar a kwanan nan a birnin Addis Abeba na kasar Habasha da wani zaman taro kafin babban taro na manyan jami'ai kan kokarin da suka shafi kawar da yunwa a nahiyar Afrika.

Tare da hadin gwiwar kungiyar FAO, sabon tsarin hadin gwiwa domin cigaban Afrika (NEPAD), kungiyar AU za ta shirya wani babban taro na manyan jami'ai a cikin watan Yuni domin duduba hanyoyin da za'a bi wajen gaggauta kokarin da ya shafi kawar da bala'in yunwa a nahiyar Afrika.

Darektan kula da cigaban karkara da noma na kungiyar AU, mista Abebe Haile-Gebriel ya nuna cewa, ko shakka babu, akwai damar kawar da yunwa a Afrika, tare kuma da yin amfani da wannan dama wajen kira da a gaggauta ayyukan cimma wannan buri ta hanyar amfani da yawan hanyoyi da dabaru da ake da su a Afrika.

Tare da bayyana cewa, ya kamata a nan gaba a cimma wani shirin dake kunshe da nagartattun ayyuka domin daidaita tsare-tsaren da ake aiwatarwa na kawar da yunwa a nahiyar Afrika. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China