in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban kasar Sin Li Yuanchao ya gana da tawagar jam'iyyar kwaminis ta kasar Afirka ta Kudu
2013-05-06 20:41:14 cri
A ranar 6 ga wata a nan birnin Beijing, memban hukumar harkokin siyasa ta kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin kuma mataimakin shugaban kasa Li Yuanchao ya gana da tawagar jam'iyyar kwaminis ta kasar Afirka ta Kudu.

A yayin ganawar, Li Yuanchao ya bayyana cewa, Sin ta dora muhimmanci kan dangantakar dake tsakaninta da kasar Afirka ta Kudu, tana son yin kokari tare da kasar Afirka ta Kudu wajen aiwatar da ayyukan da shugabannin kasashen biyu suka cimma daidaito da kuma kara yin hadin gwiwa a tsakaninsu a dukkan fannoni. Jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin tana son yin mu'amala tare da jam'iyyar kwaminis ta kasar Afirka ta Kudu a fannin fasahohin raya jam'iyyar, da inganta dangantakar dake tsakanin jam'iyyun biyu tare da dangantakar abokantaka a tsakanin kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare.

Mataimakin shugaban jam'iyyar kwaminis ta kasar Afirka ta Kudu Solly Mapaila wanda ya jagoranci tawagar jam'iyyarsa yana son kara yin mu'amala da hadin gwiwa a tsakanin jam'iyyun biyu, da koyin fasahohi daga juna, da kuma sada zumunci a tsakanin jama'ar kasashen biyu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China