in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za'a zabi sabbin shugabannin jam'iyya mai mulki a kasar Afirka ta Kudu
2012-12-17 14:31:19 cri
A ranar 16 ga wata ne, a Bloemfontein, wanda ya kasance babban birnin kasar Afirka ta Kudu a fuskar shari'a, jam'iyyar ANC wacce ta kawance daya daga cikin jam'iyyu 3 masu mulkin kasar, ta shirya gagarumin taron wakilan jam'iyar, karo na 53, domin zabar sabbin shugabanninta.

Yayin da yake gabatar da rahoton siyasa a wajen bikin bude taron, shugaban jam'iyyar ANC na yanzu, kuma shugaban kasar Afirka ta Kudu Jacob Zuma, ya ce, a cikin 'yan shekarun nan, jam'iyyarsa da sauran jam'iyyun siyasar kasar suna kokarin yin aiki kafada da kafada, inda hakan ya taimakawa kasar Afirka ta Kudu wajen samun ci gaba a fannoni da dama kamar na siyasa, tattalin arziki, diflomasiyya, al'adu da dai sauransu.

Ya ci gaba da cewa jam'iyyar ANC za ta ci gaba da jagorantar al'ummar kasar don raya tattalin arziki da masana'antu, da kuma kara samar da guraban ayyukan yi, tare da zummar kyautata zaman rayuwar al'umma.

An ce, a yayin wannan taro ne za'a zabi sabbin shugabannin jam'iyyar ANC, ciki har da sabon shugabanta.

Jam'iyyar ANC, jam'iyya ce mai mulki kuma mafi girma a kasar Afirka ta Kudu, kuma mai yiwuwa sabon shugabanta zai lashe zaben shugaban kasar a shekara ta 2014.(Murtala)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China