in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron tawagar tuntubar kasar Afirka ta Tsakiya na duniya ya yi kira ga kasar da ta fara yin shawarwari cikin hakuri
2013-05-04 16:38:02 cri
A ranar Jumma'a 3 ga wata, tawagar tuntubar kasar Afirka ta Tsakiya ta duniya ta yi taro karo na farko a birnin Brazzaville, hedkwatar kasar Kongo, inda aka zartas da "Kira ga Brazzaville", domin kalubalantar bangarori daban daban na kasar Afirka ta Tsakiya da su fara yin shawarwari tsakaninsu cikin hakuri, a kokarin tabbatar da zaman lafiya a kasar.

Shugaban kasar Kongo Brazzaville, Denis Sassou-N'guesso, shugaban kasar Afirka ta Kudu, Jacob Zuma, firaministan kasar Afirka ta Tsakiya, Nicolas Tiangaye, wakilan kungiyar AU da na MDD da dai sauransu sun halarci wannan taro.

Mahalarta taron suna ganin cewa, rikicin Afirka ta Tsakiya barazana ne ga zaman lafiya da tsaron shiyya-shiyya da ma na duniya baki daya, a sabili da haka, kamata ya yi a dauki matakai, a kokarin neman samun wani shirin share fagen warware wannan rikici na dogon lokaci.

A gun taron, an zartas da wani kuduri da aka kira "Kira ga Brazzaville", inda aka bukaci jam'iyyu daban daban na kasar da su tabbatar da yarjejeniyar siyasa ta Libreville da sanarwar N'Djamena nan take, tare da kalubalantar su dangane da farfado da yin shawarwari cikin hakuri, a kokarin samar da wani kyakkyawan yanayi, da zummar sa kaimi ga samun daidaito a duk fadin kasar.

Bisa kudurin na "Kira ga Brazzaville", tawagar za ta yi hadin gwiwa da bangarori daban daban na kasar Afirka ta Tsakiya, a kokarin samar da kariya ga fararen hula, gami da tabbatar da ba da agajin jin kai a kan lokaci, da kuma taimakawa kasar wajen sake kafa ikon tsaron kasa.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China