in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabar IMF ta nuna yabo ga bunkasuwar kasashen da suka fi samun ci gaban tattalin arziki
2013-05-03 10:08:25 cri
Shugabar asusun bada lamuni na duniya wato IMF Christine Lagarde ta bayyana wa 'yan jarida na gidan rediyo da telebijin na kasar Switzerland a ranar 2 ga wata cewa, tana nuna yabo ga bunkasuwar kasashen da suka fi samun ci gaban tattalin arziki, inda ta ce, wadannan kasashe sun taimakawa duniya baki daya wajen samun bunkasuwar tattalin arziki.

Madam Lagarde ta bayyana cewa, a halin yanzu akwai kungiyoyi uku a duniya a fannin bunkasuwar tattalin arziki. Kasashen da suka fi samun ci gaban tattalin arziki sun zama rukuni na farko, wasu kasashe kamar Amurka, Sweden, da Switzerland sun fara samun farfadowar tattalin arziki, inda suka zama rukuni na biyu. Su kuma kasashen yankuna masu amfani da kudin Euro da kasar Japan suna kokarin neman hanyar raya tattalin arziki, don haka suna cikin rukuni na uku.

Bugu da kari, Madam Lagarde ta ce, kasashen duniya suna cikin mawuyacin hali a yanzu, inda ta jaddada cewa, wajibi a dauki matakan tsuke bakin aljihu, domin ita ce kadai hanyar warware matsalar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China