in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
IMF zai bude wata sabuwar cibiyar ba da horo a Afrika
2013-04-22 10:22:47 cri

Shugaban asusun ba da lamuni na duniya IMF Christine Lagarde a jiya Lahadi ta sanar da cewa, asusun zai bude wata sabuwar cibiyar horaswa na shiyya a Afrika.

Lagarde ta sanar da hakan ne bayan wata ganawa da ta yi da jigogin asusun na nahiyar Afrika, inda a sanarwar da ta fitar, ta ce, asusun zai bude cibiya ta 6 domin ba da horon sanin makaman aiki a Accra, babban birnin kasar Ghana wanda zai taimaka gaya ma kasashen da ba su amfani da harshen Faransanci a nahiyar.

Ta kuma sanar da cewa, cibiyar koyar da sanin makaman aiki da aka bude a kasar Mauritaniya a watan Disamban shekara ta 2012 zai fara aiki a nan da 'yan watanni masu zuwa, inda zai hadu da sauran cibiyoyin a sauran sassan duniya domin taimaka ma kasashe masu tasowa su samu sanin makaman aiki a fannin shugabanci zuwa bangaren tattalin arziki da aiki da shi sosai.

Sanarwa ta kuma lura da cewa, yawancin kasashe a hamadar Sahara na Afrika na cigaba da samun karuwar al'umma, sai dai kuma ababen samun kudi a matsakaitan kasashen a nahiyar na tafiyar hawainiya, abin da ke da nasaba da yanayin kasuwanci da kasashen Turai, da wassu kasashe a arewacin nahiyar Afrika, da kuma sarkakkiyar yanayin sauyin siyasa.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China