in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yanke wa wadanda suka shirya garkuwa da mutane a Aljeriya hukuncin kisa
2013-04-24 10:17:16 cri

Wata kotu a kasar Aljeriya a ranar Talata ta yanke hukuncin kisa kan wani babban jami'in kungiyar dake da alaka da kungiyar Al-Qaida, tare da wasu 'yan ta'adda biyar duk da cewa ba su kasance a kotun ba, in ji kamfanin dillancin labaran kasar, APS.

Kotun tuhumar masu manyan laifuffuka dake Algiers ta tuhumi Mokhtar Belmokhtar da ake wa lakabi da Al-Aouer wato mai ido daya, da kasancewa cikin kungiyar 'yan ta'adda da kuma yi wa harkar tsaro a kasar zagon kasa.

Belmokhtar da wasu 'yan ta'adda guda biyar har wa yau an tuhume su da shirya da kuma gudanar da harin ta'addanci a masana'antar iskar gas ta Tiguentourine dake kudu maso gabashin kasar Aljeriya.

Ana kyautata zaton cewa, Belmokhtar shi ne ya shirya garkuwa da mutane da aka yi a masana'antar gas ta Tiguentourine a cikin watan Janairun 2013, inda hakan ya yi sanadin mutuwar 'yan kasar waje guda 38.

Rahotanni na nuna cewa, an kashe Belmokhtar da wani babban jami'in kungiyar Al-Qaida a yankin Maghreb (AQIM), Ahmed Ghedir wanda ake wa lakabi da Abu Zeid, a arewacin kasar Mali yayin wani sumame da dakarun kasar Chadi wadanda ke aiki da rundunar sojin Afirka karkashin jagorancin dakarun Faransa, suka yi a Mali cikin watan Maris.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China