in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabar IMF ta yi kira ga kasar Malawi da ta ci gaba da yin kwaskwarima ga tattalin arzikinta
2013-01-06 17:58:47 cri
A Jiya Asabar 5 ga wata, shugabar asusun ba da lamuni na duniya wato IMF Christine Lagarde ta yi kira ga kasar Malawi da ta ci gaba da yin tsayin daka kan yi wa tattalin arzikinta kwaskwarima, duk da yake kasar na fuskantar matsalar hauhawar farashin kayayyaki bayan da ta aiwatar da shirin gyare-gyare kan tattalin arziki da ke karkashin jagorancin kasashen yamma.

Tun daga ranar 4 ga wata ne, Madam Lagarde ta fara ziyarar aiki na kwanaki biyu a kasar Malawi inda a lokacin wani dandalin tattaunawar da aka shirya ta yaba wa gwamnatin kasar Malawi bisa ga kyawawan sakamakon da ta samu a cikin aikin gyare-gyaren tattalin arziki da take gudanarwa, wanda ya maido da odar tattalin arzikin kasar yadda ya kamata.

Madam Lagarde ta kuma yi fatan ganin Malawi za ta ci gaba da inganta wannan aiki, sannan raya tattalin arzikinta a fannoni daban daban a maimakon dogaro bisa ayyukan gona kawai.

A nata bangaren, shugabar kasar ta Malawi Joyce Banda ta yi alkawarin cewa, ko da yake aikin gyare-gyare yasa jama'ar ta cikin wani halin kunci, duk da haka gwamnati ba za ta yi watsi da wannan shiri ba domin ana sa ran ganin farfadowar tattarlin arzikin kasar a karshen wannan shekarar da muke ciki.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China