in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane fiye da 200 sun rasa rayukansu sakamakon bala'in girgizar kasa a Lushan
2013-04-21 16:25:11 cri

Bisa kididdigar baya-bayan nan da ma'aikatar kula da harkokin jama'a ta kasar Sin ta bayar, an ce, ya zuwa karfe 10 na ranar Lahadi 21 ga watan nan da safe, yawan mutanen da suka rasa rayukansu da wadandan suka bace sun kai 203, baya ga wadanda suka jikkata da yawansu ya kai kusan dubu 11 da dari 5, ciki har da mutane 960 suka ji rauni matuka sakamakon bala'in girgizar kasa da ya auku a gundumar Lushan na yankin birnin Ya'an dake lardin Sichuan.

Li Keqiang, firaministan kasar Sin wanda ke ba da jagoranci ga aikin ceto a gundumar Lushan, inda aka samu bala'in mafi tsanani, ya jaddada cewa, dole ne a sanya aikin ceto mutane a gaban kome. Sannan ya alkawarta cewa, gwamnati za ta taimakawa jama'a wadanda bala'in ya aukuwa wajen sake gina gidajensu.

Bisa labarun da muka samu, an ce, bayan aukuwar bala'in girgizar kasa a gundumar Lushan, kasashen duniya, kamar su Amurka, Rasha, Japan, Bribaniya, Faransa, Cuba da dai sauransu sun nuna jajantawa gwamnatin kasar Sin, inda suka yabawa matakan ceton jama'a da gwamnatin kasar Sin ta dauka a kan lokaci, kuma suka bayyana cewa, suna fatan za su iya ba da tallafi ga jama'ar da suke fama da radadin wannan bala'in. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China