in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Afirka sun yi Allah wadai da fashewar boma-bomai a kasar Amurka
2013-04-17 10:31:23 cri
Lamarin fashewar boma-boman na birnin Boston, ya jawo hankalin kasa da kasa a nahiyar Afirka. Inda shugaban kasar Nijeriya Goodluck Jonathan, ya yi jawabi a ranar 16 ga wata, yana mai cewa, wannan mummunan al'amari ya saba wa 'yancin dan Adam.

Hakazalika kuma, ministan kula da harkokin wasanni na kasar Zimbabwe David Coltart, ya yi tir da wannan lamari, da ma duk wani irin harin ta'addanci wanda ke kawo barazana ga jama'a. Bugu da kari an nuna rashin amincewa da irin wannan hari da aka kaiwa gasar motsa jiki, wadda bata da nasaba da siyasa ko kadan.

Har ila yau, kafofin watsa labaru na kasar Kenya sun bada sharhi cewa, kungiyar 'yan wasan kasar Kenya ta ci nasara a gasar gudun yada-kanin-wani ta mata a birnin Boston, sai dai sa'a daya da hakan ne fashewar boma-bomai ta auku, lamarin ya maida gasar tamkar wani bala'i, don haka dai jama'a, ba za su iya kawar da damuwar da wannan lamarin ya kawo daga zuciyarsu cikin kankanin lokaci ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China