in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na M.D.D. ya yi Allah wadai da hare-haren boma-bomai da aka kai a hedkwatar kasar Somaliya
2013-04-16 11:10:41 cri

A ranar 14 ga wata, dakarun dauke da makamai sun fara kai hare-haren bom da na kunar bakin wake ga ofisoshin tafiyar da mulki, da babban ginin kotun kasar, da babban filin jiragen kasa da ke birnin Mogadishu, hedkwatar kasar Somaliya, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane a kalla 24. Haka kuma, dakarun dauke da makamai da ke adawa da gwamnatin kasar Somaliya na Al-shabaab sun bayyana daukar alhakin kai hare-haren boma-bomai a wannan rana.

A ranar 15 ga wata, kwamitin sulhu na M.D.D. ya ba da sanarwa cewa, dakarun dauke da makamai da ke adawa da gwamnatin na Al-shabaab sun dauki alharin kai hare-haren ta'addanci, kuma kwamitin sulhu na M.D.D. ya yi Allah wadai da wannan lamari da kakkausan harshe.

Kwamitin sulhu na M.D.D. ya sake nanata cewa, duk ayyukan ta'addanci, laifuffuka ne da za a hukunta wa, haka kuma ya sake jaddada cewa, kwamitin sulhu na M.D.D. yana shirin daukar matakai game da wadannan mutane da suka kawo kalubale game da zaman lafiya da karko a kasar Somaliya, sannan kuma ya nuna goyon baya game da yunkurin samar da zaman lafiya da sulhu a kasar Somaliya.

Ban da wannan kuma, a ranar 15 ga wata, sakatare janar na M.D.D. Ban ki-moon ya ba da wata sanarwa, inda ya ce, ya ba da tabbaci cewa, wadannan aika-aikar ba za su kawo sauyi ga niyyar jama'ar Somaliya ta neman samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar Somaliya ba.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China