A ranar 16 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya buga waya ga shugaban kasar Amurka Barack Obama, inda ya jajantawa gwamnatin kasar Amurkan, da jama'arta sakamakon faruwar lamarin na fashewar boma-bomai a birnin Boston.
Shugabannin kasashen Rasha, Koriya ta kudu, da Jamus, da sauran kasashen duniya su ma sun yi tir da wannan lamari.(Zainab)