in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tattalin arzikin kasashen Afirka zai ci gaba da bunkasa, a cewar bankin duniya
2013-04-16 10:54:15 cri
Bankin duniya ya yi hasashe a ranar 15 ga wata cewa, yankin Afirka dake kudu da hamadar Sahara na da kyakkyawar makoma a fannin tattalin arziki, amma ana bukatar karin manufofi don kawar da talauci a yankin ta hanyar yin amfani da bunkasuwar tattalin arzikinsa.

Bankin duniya ya gabatar da wani rahoto game da makomar tattalin arziki a nahiyar Afirka a wannan rana, inda ya bayyana cewa, kashi daya cikin kashi hudu na kasashen yankin Afirka dake kudu da hamadar Sahara sun samu karuwar tattalin arziki fiye da kashi 7 cikin kashi dari, inda wasu daga cikinsu suka kasance kasashe mafi samun bunkasuwa a fadin duniya.

A sakamakon farfadowar tattalin arzikin duniya da karuwar bukatun cikin gida, tattalin arzikin kasashen Afirka zai ci gaba da samun karuwa.

Hakazalika, bankin duniya ya nuna cewa, a shekaru fiye da 10 da suka wuce, bunkasuwar tattalin arziki na taimakawa kasashen Afirka wajen kawar da talauci, amma matsalolin rashin daidaici da kara dogora da albarkatun kasa yayin da ake raya tattalin arziki sun kawo cikas ga kawar da talauci a kasashen Afirka ta hanyar yin amfani da bunkasuwar tattalin arzikinsu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China