in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashe da dama na nahiyar Afirka dake kudu da hamadan Sahara suna fuskantar hauhawar farashin kaya
2011-04-25 14:38:37 cri
A ran 25 ga wata, sashen kula da harkokin ciniki na ofishin jakadan Sin dake kasar Kenya ya bayar da wani labari, inda ya ce, kasashe da dama na nahiyar Afirka dake kudu da hamadan Sahara suna fuskantar hauhawar, farashin kaya musamman abinci da makamashi day a karu sosai.

Bisa kididdigar tattalin arziki ta watan Maris da kasashen Afirka dake kudu da hamadan Sahara suka bayar, an ce, kasashen Afirka ta kudu, Nijeriya, Kenya, Uganda, da kuma Tanzania suna fuskantar hauhawar farashin kaya. Yawan hauhawar farashin kaya na kasar Kenya ya karu watanni 5 da suka gabata, yawansa na watan Maris ya kai kashi 9.19 cikin kashi dari, a ciki, farashin gidaje, ruwan sha, wutar lantarki, abinci da kuma makamashi sun fi samun karuwa.

Manazarta sun bayyana cewa, yanayin hauhawar farashin kaya zai kawo illa ga zaman rayuwar jama'a da kamfanoni kanana da matsakaita a kasashe da dama dake kudu da hamadan Sahara, kana zai kawo cikas ga samun bunkasuwar tattalin arzikinsu a wannan shekarar, da kuma haddasa rikice-rikice a fannin siyasa. Yanzu dai, wasu kasashe sun riga sun dauki matakai don tinkarar hauhawar farashin kaya.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China