in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Afirka da ke Hamadar Sahara ta kudu na samun sabuwar damar ci gaban tattalin arziki
2011-08-04 14:43:36 cri

Manazarta suna ganin cewa, idan kasashen Afirka da ke Hamadar Sahara ta kudu sun iya kara karfafa zuba jari da yin kokarin warware matsalar yawan al'umma, da yasa dimbin jama'a rasa guraban aikin yi, da bala'in fari, da matsalar makamashi, kana da koma bayan muhimman abubuwan more rayuwar jama'a, to za su taka wani sabon mataki na farfadowar tattalin arzikinsu. Alal misali, kafin gwamnatin kasar Kenya ta kudura aniyyar raya fannin sadarwa, dole sai mutune sun yi jerin gwano in har zasu buga waya a akwatin waya na kan hanya, amma a halin yanzu gidaje fiye da miliyan 5.5 na kasar suna amfani da wayar salula.

A kwanan nan, wani shahararren kamfanin kula da ayyukan zuba jari na kasar Amurka ya bayar da rahoto cewa, ko da yake kasancewar dimbin matasa a kasashen Afirka da ke Hamadar Sahara ta kudu wani kalubale ne gare su,duk da haka suna iya jawo jarin da ke bukatar dimbin mutane, ta yadda za a sa kaimi ga ci gaban tattalin arzikin wurin. Haka zalika kuma, yaduwar fasahar ban ruwa za ta inganta bunkasuwar tattalin arziki sakamakon kasancewar yawancin manoma na fama da karancin ruwa a gonarsu.Gwamnatin kasar Kenya tana kokarin yiwa tsarin ban ruwa kwaskwarima, kuma ta kebe kudi Dala miliyan 22 domin gina madatsar ruwa, duk a kokarin samun ci gaba.

Bisa kididdigar da aka bayar, an ce, a cikin shekaru 10 da suka gabata, matsakaiciyar jimillar GDP da kasashen Afirka 49 da ke Hamadar Sahara ta kudu sukan samu na karuwa da kashi 5.7 cikin kashi dari a ko wace shekara.(Kande)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China