in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ayarin jiragen ruwan soja na Sin ya kammala ziyara a Morocco
2013-04-14 17:02:05 cri
A yammacin ranar Asabar 13 ga wata nan ne ayarin jiragen ruwan soja na 13 na kasar Sin, ya tashi daga tashar jirgin ruwa ta Casablanca dake kasar Morocco, bayan kammala ziyararsu ta kwanaki 5, domin sada zumunci a karo na farko a kasar ta Morocco.

A yayin ziyarar, mai ba da umurni ga ayarin, manjo Li Xiaoyan, ya gana ga manyan jami'ai, da kwamandojin kasar, inda ya gabatar musu da yanayin da ake ciki na ba da kariya ga jiragen ruwa a mashigin Aden, wanda ke yankin tekun Somaliya, da jiragen ruwan sojan Sin suka yi cikin shekaru 4 da suka wuce, da kuma yanayin da ake ciki na yaki da 'yan fashin teku a yanzu. Dadin dadawa ya yi shawarwari da su kan kara karfafa mu'amala da hadin gwiwa, tsakanin jama'a da sojojin kasashen biyu, inda bangarorin biyu suka bayyana cewa, ziyarar ayarin jiragen ruwan sojan Sin a karo na farko, za ta karfafa dankon zumunci a tsakanin jama'ar kasashen biyu yadda ya kamata.

Bugu da kari, a yayin ziyarar, sojojin ruwan Sin da na Morocco, sun kai ziyara ga jiragen ruwan juna, tare da gudanar da gasar kwallon kwando. Har ila yau sojojin sun yi musayar ra'ayoyi kan ayyukan kiyaye tsaron kasa a yankin teku, inda sojojin ruwan Sin suka gabatar da fasahohinsu, na ba da kariya ga zirga-zirgar jiragen ruwa a teku, yayin da takwarorinsu na Morocco, suka gabatar da fasahohin yaki da yin fasa-kwaurin kwayoyi, da safarar bil'adama,da kuma yaki da gurbata ruwan teku da sauransu.

Morocco ta kasance wuri na uku, da ayarin jiragen ruwan soja na 13 na Sin ya kai ziyara. Kafin wannan, ayarin ya kai ziyara a Malta da Aljeriya, kuma zai kai ziyara a Portugal da Faransa a nan gaba.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China