in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan da Sudan ta Kudu sun nanata aniyarsu ta aiwatar da yarjejeniyar tsaro a tsanake
2013-04-13 16:46:08 cri
Ranar 12 ga wata, shugaba Omer Hassan Ahmed Elbashir na kasar Sudan da ke ziyara a birnin Juba, hedkwatar kasar Sudan ta Kudu da kuma takwaransa Salva Kiir Mayardit na Sudan ta Kudu sun nanata cewa, kasashen 2 za su dauki hakikanin matakai domin aiwatar da yarjejeniyar tsaron da suka daddale, tare da sa aya ga bayar da ko wane irin goyon baya da kariya ga dakarun masu adawa da gwamnati da ke fadi-tashi ma juna.

A yayin taron manema labarun da suka shirya cikin hadin gwiwa bayan shawarwari, shugabannin 2 sun jaddada cewa, tabbatar da samun tsaro, wani tushe ne wajen yin hadin gwiwa a tsakanin kasashen 2, ta haka kasashen 2 za su himmantu wajen aiwatar da dukkan tanade-tanaden da ke cikin yarjejeniyar tsaron. Sa'an nan shugabannin 2 sun yaba wa juna kan matakan kokarin kafa yankin rashin daukar matakin soja a kan iyakarsu, sun kuma jaddada muhimmancin tawagar sa ido da kungiyar tarayyar kasashen Afirka wato AU ta tura, wadda za ta sa ido kan aiwatar da yarjejeniyar tsaron.

Har ila yau shugabannin 2 sun nuna cewa, za su aiwatar da yarjejeniyar hadin gwiwa da suka daddale a birnin Addis Ababa, a watan Satumba a bara, a kokarin inganta huldar da ke tsakanin kasashensu ta fuskar siyasa, tattalin arziki da cinikayya, za su kuma ci gaba da kokarinsu na warware dukkan batutuwan da ba su warware ba tukuna. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China