in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi maraba da shawarwarin da ke tsakanin shugabannin Sudan da Sudan ta Kudu
2013-04-13 16:45:03 cri
Ranar 12 ga wata, ta bakin kakakinsa Ban Ki-moon, magatakardan MDD ya ba da wata sanarwa, inda ya yi maraba da gudanar da shawarwari a tsakanin shugabannin kasashen Sudan da Sudan ta Kudu a wannan rana a birnin Juba, hedkwatar kasar Sudan ta Kudu.

A cikin sanarwarsa, Ban Ki-moon ya ce, ya ji farin ciki sosai da ganin Sudan da Sudan ta Kudu sun yi kyakkyawan shawarwari domin aiwatar da yarjejeniyoyin da suka daddale a birnin Addis Ababa a ran 27 ga watan Satumba a shekarar bara. Sa'an nan ya yaba wa shugabannin na kasashen 2 bisa aniyarsu ta ci gaba da himmantuwa wajen warware batun yankin Abyei, ya kuma kalubalance su kawar da sabani a tsakaninsu dangane da matsayin karshe na yankin na Abyei.

Har wa yau Ban Ki-moon ya yi maraba da maido da fitar da man fetur a tsakanin kasashen 2, a cewarsa kuma, lamarin ya kasance wata muhimmiyar alama ce ta daban a fannin kokarin maido da dangantakar da ke tsakaninsu yadda ya kamata, baya ga kafa yankin rashin daukar matakin soja a tsakaninsu da kuma gudanar da tsarin yin bincike da sa ido a kan bakin iyakarsu cikin hadin gwiwa. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China