in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Syria ta bukaci MDD da ta sanya 'yan tawayen kasar cikin jerin kungiyoyin ta'addanci
2013-04-12 16:22:07 cri
Bisa labarin da kamfanin dillancin labarai na Syrian Arab ya bayar ran 11 ga wata, an ce a wannan rana, gwamnatin kasar Syria ta gabatar wa babban sakataren MDD da shugaban kwamitin sulhu da wata wasika, inda ta bukaci MDD ta tsai da kudurin sanya kungiyar adawa ta kasar "Victory Front" cikin jerin kungiyoyin 'yan ta'adda daidai da kungiyar Al-Qaeda, da daukar mata hukunci, bisa kudurorin MDD da dokokin kasa da kasa.

Cikin wasikar, ma'aikatar harkokin wajen Syria ta bayyana cewa, shugaban kungiyar "Victory Front" ya taba bayar da jawabin bautawa kungiyar Al-Qaeda, wannan ya tabbatar da cewa, akwai alaka tsakanin kungiyoyin biyu, dalilin da ya sa, Syria ta bukaci MDD ta hukunta kungiyar "Victory Front" bisa kudurorin lamba 1267 da 1989 na kwamitin sulhu na MDD. Ma'aikatar ta kuma yi gargadin cewa, idan gamayar kasa da kasa ba su mai da hankali kan kungiyar adawa ta kasar Syria ta "Victory Front" da kuma magoyon bayanta ba, to za a fuskanci sakamako mai tsanani.

Kuma bisa labarin da aka samu, ran 9 ga wata, shugaban reshen kungiyar Al-Qaeda da ke kasar Iraq Baghdadi ya bayyana cewa, kungiyar "Victory Front" ta riga ta hada kai tare da kungiyarsa, shugaban kungiyar Ciorani ya sanar da bauta wa shugaban kungiyar Al-Qaeda Ayman al-Zawahri ran 10 ga wata. Bugu da kari, bisa kudurin MDD, duk wadanda suka kulla hulda da kungiyar Al-Qaeda, ya kamata gamayyar kasa da kasa ta rike kudade da kadarorinsu, hana su tafiye-tafiye, da dakatar da ba su makamai. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China