in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD zata baiwa shirin tattaunawa don gane da rikicin Syria goyon baya
2013-03-03 16:31:42 cri
Manzon musamman na MDD da tarayyar Larabawa don gane da rikicin kasar Syria Lakhdar Brahimi, da babban sakataren majalissar Ban Ki-Moon, sun bayyana aniyar baiwa batun tattaunawa tsakanin wakilan gwamnatin Syria, da na 'yan tawayen kasar cikakken goyon baya.

Wata takardar bayan taro da suka sanya wa hannu bayan kammalar taron da suka gudanar a birnin Pelerin na kasar Switzerland, jami'an biyu sun bayyana takaicin yadda yunkurin warware wannan matsala ya ci tira a baya.

Daga nan sai suka nanata aniyar kasashen duniya, don gane da tsayawa tsayin daka, wajen kawo karshen wadannan kiki-kaka ta hanyar lumana, tare da kiyaye harkokin dukkanin al'ummar kasar.

Har ila yau, sakataren majalissar dinkin duniyan da Lakdar Birahimi, sun nuna rashin jin dadin su ga yadda a cewar su, tsagin gwamnatin Syria, dama na 'yan tawayen kasar ke dada watsi da batun martaba rayukan bil'adama a kasar, suna masu karfafa muhimmancin dake akwai, na baiwa batun hukunta laifukan yaki da cin zarafin bil'adama kulawa yadda ya dace. (Saminu Usman)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China