in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Uhuru Kenyatta ya yi rantsuwar kama aiki a matsayin shugaban kasar Kenya
2013-04-10 15:24:52 cri

Ranar 9 ga wata, Uhuru Kenyatta wanda ya lashe zaben zama shugaban Kenya ya yi rantsuwar kama aikinsa a birnin Nairobi hedkwatar kasar, ke nan ya zama shugaba na hudu tun bayan da kasar ta samu 'yancin kai.

A cikin jawabinsa, Uhuru Kenyatta ya bayyana cewa a cikin wa'adinsa na shekaru biyar, zai yi kokarin cika al'akwarin da ya yi wa jama'ar Kenya ta hanyar samar da guraben aikin yi da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arziki, tare kuma da kara zuba jari ga sha'anin ba da ilmi, ba da jiyya, sha'anin noma da sauransu. A sa'i daya kuma, sabon shugaban kasar Kenya cewa ya yi zai kara hadin gwiwa da kasashe dake makwabtaka da kasar Kenya a kokarin sa kaimi dunkulewar tattalin arzikin Afrika.

Uhuru Kenyatta dai ya lashe zaben shugaban kasar Kenya da aka yi a ran 4 ga watan Maris bisa yawan kuri'un da ya samu na kashi 50.07 bisa dari. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China