Xi Jinping ya ake da sakon jaje ga shugaban Brazil
2022-02-18 19:21:38 CRI
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya aikewa takwaransa na Brazil Jair Bolsonaro da sakon jaje, bisa mamakon ruwan sama da ya haifar da hasarar rayuka a kasar sa.
Ya zuwa jiya Alhamis, ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka shafe kwanaki ana yi, ya haddasa ambaliya, da zaftarewar kasa a birnin Petropolis na kasar, lamarin da ya sabbaba rasuwar a kalla mutane 117, baya ga wasu karin mutanen 116 da suka bace. (Saminu)