‘Yan Wasan Afirka Na Yayata Ruhin Olympics A Beijing
2022-02-11 20:47:33 CMG
Ko wata kasa da bata da yanayin kankara za ta iya tura ‘yan wasa su halarci gasa ta matsayin koli na wasannin kankara, wato gasar Olympics ta lokacin hunturu? To, wasu kasashe 5 dake nahiyar Afirka sun ba da amsa da “E” ga wannan tambaya. wadannan kasashe sun hada da Najeriya, da Eritrea, da Morocco, da Ghana, da kuma Madagascar. Wadannan kasashe sun tura ‘yan wasa 6 don halartar wasannin Olympics na lokacin hunturu karon 24 dake gudana a birnin Beijing na kasar Sin.