logo

HAUSA

ECOWAS ta dakatar da Burkina Faso daga zama mambarta

2022-01-29 17:03:57 CRI

ECOWAS ta dakatar da Burkina Faso daga zama mambarta_fororder_f3d3572c11dfa9ece4244522a9bb3d0a918fc176

Kungiyar raya tattalin arzikin yammacin Afrika ECOWAS, ta sanar da dakatar da Burkina Faso daga matsayinta na mamba, saboda juyin mulkin sojoji a kasar.

An dauki wannan mataki ne biyo bayan taron shugabannin kasashen yankin da aka yi ta kafar bidiyo a jiya Juma’a.

A ranar Litinin ne, rundunar sojin Burkina Faso ta sanar ta kafar talabijin cewa, sojoji sun kwace mulki tare da kawo karshen ayyukan shugaban kasar Roch Marc Christian Kabore.

Sanarwar bayan taron shugabannin ECOWAS ta ruwaito cewa, sojojin sun tilastawa shugaba Kabore yin murabus, inda suka nemi sojojin su sake shi, tare da sauran ‘yan siyasar dake tsare.

A cewar sanarwar, za a tura tawagogin kungiyar biyu karkashin kwamitin manyan hafsoshinta da majalisar ministoci zuwa Burkina Faso, domin tantance yanayin tsaro da siyasar kasar.

Bugu da kari, shugabannin na kasashen ECOWAS, za su kara haduwa a Accra babban birnin Ghana a ranar Alhamis, domin sake nazarin yanayin kasashen Burkina Faso da Guinea da Mali. (Fa’iza Mustapha)