logo

HAUSA

Gwamnatin Najeriya ta kawo karshen dakatarwar da ta yiwa Twitter na tsawon watanni 7

2022-01-13 20:38:34 CMG

Gwamnatin Najeriya ta kawo karshen dakatarwar da ta yiwa Twitter na tsawon watanni 7_fororder_Nigerian gov

Gwamnatin Najeriya ta kawo karshen dakatarwar da ta yi wa shafin sada zumunta na Twitter, watanni bakwai bayan da ta dakatar da gudanar da ayyukan kamfanin da ke Amurka, a kasar mafi yawan al’umma a nahiyar Afirka.

Babban darektan hukumar fasahar sadarwa ta kasar Kashifu Abdullahi, ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, dage haramcin da aka yiwa kamfanin a Najeriya zai fara aiki ne daga karfe 12 na safiyar yau Alhamis agogon kasar, bayan da kamfanin ya amince da cika dukkanin sharuddan da gwamnatin Najeriya ta gindaya masa.(Ibrahim)

Ibrahim