Ministan harkokin wajen Sin ya gana da takwaransa na Sri Lanka
2022-01-10 10:01:07 CRI
Mamban majalisar gudanarwar kasar Sin kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, wanda ke ziyara a Sri Lanka, ya gana da ministan harkokin wajen kasar, G.L Peiris, a jiya Lahadi, inda ya lashi takobin kasarsa za ta hada hannu da Sri Lanka, wajen adawa da siyasantar da annobar COVID-19 da batun gano asalinta. (Fa’iza Mustapha)