Babban hafsa mai kula da sojojin Sudan: Za a kafa sabuwar gwamnati
2021-10-26 20:58:43 CMG
A yau Talata, babban hafsa mai kula da sojojin kasar Sudan, Janar Abdel Fattah al-Burhan, ya kira wani taron manema labaru a Kartoum, fadar mulkin kasar, inda ya yi alkawarin cewa, za a kafa sabuwar gwamnati, ta wata hanyar da za ta gamsar da dukkan jama’ar kasar. (Bello Wang)