Li Keqiang ya halarci taro na 24 na jagororin Sin da ASEAN
2021-10-26 19:47:50 CRI
Firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya halarci taro na 24 na jagororin Sin da kungiyar ASEAN, wanda ya gudana da yammacin Talatar nan daga birnin Beijing.
Shugaban masarautar Brunei, wanda ke rike da jagorancin kungiyar ASEAN na karba karba, da shugabannin Cambodia, da Indonesia, da Laos, da Malaysia, da Philippines, da Singapore, da Thailand, da Vietnam sun halarci taron. (Saminu)