Masanin Birtaniya: Kokarin tabbatar da ci gaban al’umma ya nuna yadda Sin ke sauke nauyi bisa wuyanta wanda kasashen yamma suka kasa yi
2021-10-09 17:26:18 CRI
Martin Jacques, wani sanannen masanin kasar Birtaniya, ya bayyana yayin wata tattaunawa a kwanan nan cewa, duk da cewa kasashen yammacin duniya, musamman Amurka, suna fuskantar matsalar rata tsakanin masu arziki da matalauta, sai dai wadannan kasashe sun gaza yin wani abin a zo a gani don sauke nauyin da ya dace wajen warware wadannan matsaloli. Amma sabanin hakan, kasar Sin tana kokarin bin hanyoyin warware matsalar rashin daidaito ta hanyar kyautata tsarin samar da makoma ta bai daya. Tana yin abubuwan da ya kamata a ce kasashen yamma ne ke yi amma suka gaza yi.(Ahmad)