Tunawa da cika shekaru 100 da kisan kiyashi da aka yi wa bakaken fata a birnin Tulsa
2021-06-01 20:58:38 CRI
A jiya ne, al’ummar birnin New York su ka gudanar da bikincika shekaru 100 da kisan kiyashi da aka yi wa bakaken fata a birnin Tulsa dake jihar Oklahoma. Tulsa, shi ne birni na biyu mafi girma a jihar Oklahoma, wanda ya samu saurin ci gaba a farkon karni na 20 bayan da aka gano man fetur a wurin. A ranar 1 ga watan Mayun shekarar 1921, wasu mahara fararen fata suka cinna wuta a unguwar Greenwood da ke birnin, inda aka halaka bakaken fata kimanin 300 da suka hada da mata da yara.(Lubabatu)