An shiga mako na biyu da Isra'ila take kai hare hare ga zirin Gaza
2021-05-18 08:53:09 CRI
A jiya Litinin ne aka shiga mako na biyu da Isra’ila take kai hare-hare ga zirin Gaza. Kakakin sashen kula da lafiya da ke zirin Gaza ya bayyana a wannan rana cewa, hare-haren da sojojin Isra’ila suka fara kaddamarwa tun daga ranar 10 ga wata sun halaka Palasdinawa 198, ciki har da yara 58 da kuma mata 35, a yayin da wasu 1300 suka ji raunuka.(Lubabatu)