logo

HAUSA

Aminu Inuwa Darma: Ya kamata matasan Najeriya su tashi tsaye don gina kasa

2021-05-18 14:31:20 CRI

Aminu Inuwa Darma: Ya kamata matasan Najeriya su tashi tsaye don gina kasa_fororder_微信图片_20210518110802

Aminu Inuwa Darma, dan asalin karamar hukumar Kumbotso dake jihar Kanon Najeriya ne, wanda a yanzu haka yake karatun neman digiri na uku a kwalejin nazarin ilimin noma ta kasar Sin dake Beijing.

A yayin zantawar sa da Murtala Zhang, Aminu Darma ya bayyana ra’ayinsa kan bambancin tsarin ilimin dake kasancewa tsakanin kasar Sin da kasar Najeriya.

Aminu Inuwa Darma: Ya kamata matasan Najeriya su tashi tsaye don gina kasa_fororder_微信图片_20210518110755

Ya kuma bayyana yadda kasar Sin ta samu babban ci gaba a fannin dakile cutar mashako ta COVID-19, musamman karkashin jagorancin jam’iyyar kwaminis ta kasar, inda ya ce jam’iyya ce mai lura da moriyar al’umma gami da cusawa al’umma akidar kishin kasa.

A karshe, malam Aminu Darma ya yi kira ga matasan Najeriya da ma duk Afirka baki daya, su tsahi tsaye don nuna jajircewa wajen gina kasashen su. (Murtala Zhang)