Musulmai a Kashgar na Xinjiang sun yi sallar Juma’a ta farko a watan azumi
2021-04-17 16:18:24 CRI
Jiya Jumma’a 16 ga wata, musulmai a birnin Kashgar na jihar Xinjiang dake kasar Sin sun yi sallar Jumma’a ta farko a watan azumi.
A wannan rana musulmai a birnin sun shiga masallacin Id Kah, wanda ya kasance masallaci mafi girma a jihar Xinjiang, domin yin salla.
Masallacin Id Kah, wanda aka gina shi a shekarar 1442, yana yammacin filin Id Kah na birnin Kashgar.(Jamila)