Jakadan Najeriya a Sin: Yadda Sin ta yi nasarar yaki da fatara zai zama abin koyi ga kasashen da ke da burin kyautata rayuwar al’ummominsu
2021-03-05 21:15:21 CRI
A yau ne, aka bude taron shekara shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ta NPC a birnin Beijing. Wakiliyarmu Kande ta zanta da jakadan Tarayyar Najeriya da ke kasar Sin Baba Ahmad Jidda bayan da ya halarci bikin bude taron, inda Jakadan ya bayyana cewa, rahoton aikin gwamnati da firaminista Li Keqiang ya gabatar ya burge shi sosai, yana mai cewa, yadda kasar Sin ta yi nasarar yaki da fatara, zai zama abin koyi ga Najeriya da ma sauran kasashen da ke da burin kyautata rayuwar al’ummominsu.