Kasashe 5 sun shirya rawar daji mai take "Zaman Lafiya-21" a yankin teku na Pakistan
2021-03-01 16:17:33 CRI
A makon jiya, wata tawagar jiragen ruwan yaki ta kasar Sin wadda ke kunshe da jiragen ruwan yaki uku ta halarci wata rawar daji mai take “Zaman lafiya-21” da kasashen Pakistan da Rasha da Amurka da Birtaniya da Sin suka shirya tare a yankin teku na Pakistan, inda suka yi rawa a fannonin ceto da tsara ayarin jiragen ruwa daban daban bisa umurni da dai makamantansu. (Sanusi Chen)