logo

HAUSA

Dr. Muhammad Sulaiman Abdullahi: Ina alfahari da koyawa daliban kasar Sin harshen Hausa

2020-06-23 13:26:21 CRI

Dr. Muhammad Sulaiman Abdullahi: Ina alfahari da koyawa daliban kasar Sin harshen Hausa

Dr. Muhammad Sulaiman Abdullahi, malami ne a sashin koyar da harsunan Najeriya dake jami'ar Bayero a jihar Kano ta Najeriya. Kuma a halin yanzu, yana koyar da harshen Hausa ga wasu daliban kasar Sin dake karatu a jami'ar koyon harsunan waje ta Beijing, wato BFSU a takaice.

Dr. Muhammad Sulaiman Abdullahi: Ina alfahari da koyawa daliban kasar Sin harshen Hausa

Dr. Muhammad Sulaiman Abdullahi ya bayyana cewa, daliban kasar Sin suna da kwazo matuka wajen koyon yaren Hausa da al'adun gargajiya na Hausawa, kuma a cewarsa, gwamnatin kasar Sin na iyakacin kokarinta wajen karfafa dankon zumunta da kasashen Afirka, ciki har da Najeriya.(Murtala Zhang)