logo

HAUSA

Likitan Najeriya: Za a kawo karshen annobar Corona a kasar Sin

2020-02-14 20:55:15 CRI

Likitan Najeriya: Za a kawo karshen annobar Corona a kasar Sin

 

Yayin da ake kokarin dakile yaduwar cutar Corona a kasar Sin, Bello Wang ya samu yin hira da Dr. LOSKURIMA Umar, likitan dake aiki a asibitin koyarwa na jami'ar Maiduguri ta Najeriya, don kwararren likitan ya bayyana matakan da ya kamata a dauka a Najeriya don tinkarar yiwuwar bullar wannan annoba. Ban da wannan kuma, a cikin wannan shiri, akwai hirar da aka yi da Abdulsalam Aji Suleiman, wanda ke karatun digiri na 3 a jami'ar kimiyya da fasaha ta Huazhong dake birnin Wuhan na kasar Sin, inda ake fi fama da cutar Corona a wannan karo. Dalibin ya bayyana yanayin da 'yan Najeriya wadanda ke zama a birnin Wuhan suke ciki.(Bello Wang)