Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Ministan harkokin wajen Sin zai kira taron manema labarai a gobe Lahadi
2020-05-23 20:44:38        cri
Da misalin karfe 3 na yammacin gobe Lahadi, za a shirya taron manema labarai a babban dakin taron jama'a dake birnin Beijing, inda wakilin majalisar gudanarwa, kana ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, zai amsa tambayoyin 'yan jarida na kasar Sin da na kasashen ketare za su yi masa, game da batutuwan dake shafar manufofin diflomasiyyar Sin da kuma dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen ketare.

A lokacin kuma, sashen Hausa na babban gidan rediyo da talabijin na kasar Sin (CMG) zai watsa labaran taron ta shafin intanet da shafinsa na FACEBOOK kai tsaye. (Maryam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China