Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kakakin Sin: Sin na tsayawa tsayin daka wajen kare rayuka
2020-05-09 17:22:51        cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana cewa, kasar Sin tana tsayawa tsayin daka kan ka'idar daukar aikin kare rayuka a mastayin abu mafi muhimmanci, a lokacin da take fuskantar yaduwar cutar numfashi ta COVID-19 a kasar. Ta ce kasar Sin tana son hada gwiwa da Amurka domin kawo karshen yakin cikin sauri, don haka, ya dace bangarorin biyu su ajiye sabaninsu kan harkokin siyasa, su mai da hankali kan kiyaye al'ummomin kasashensu yadda ya kamata.

A kwanakin baya, ministan harkokin wajen Amurka Mike Pompeo, ya zargi manufofin siyasar kasar Sin, inda ya ce, kalubalen da Amurka ke fuskanta na da nasaba da mulkin jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin. Dangane da wannan tsokaci, Hua Chunying ta bayyana yayin taron manema labarai da aka yi a jiya cewa, jami'in na Amurka ya ce, jam'iyyar kasarsa tana da bambanci da ta kasar Sin, tana mai cewa, lallai akwai bambanci guda daya da aka amince da shi, wato jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin tana mai da hankali matuka kan kiyaye al'ummarta da ma rayuwarsu. Ta ce, JKS tana mutunta ko wani rai, ta na kuma yin iyakacin kokarinta wajen jinyar dukkanin al'ummomin kasar da suka kamu da cutar COVID-19, daga tsoho mai shekaru 108 zuwa jariri, tana kuma samar musu jinya ba tare da sun biyan kudi ba. Ta ce, a lardin Hubei, an yi jinyar jimilar tsofaffi 3,600 da suka kamu da cutar, wadanda shekarunsu ya haura 80. (Maryam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China