Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
An kadammar da jerin taruka ta kafar bidiyo tsakanin bangarorin Sin da Afirka don musayar dabarun dakile cutar COVID-19
2020-04-27 20:15:03        cri
Geng Shuang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, ya furta a yau Litinin cewa, ma'aikatarsa ta yi hadin gwiwa tare da hukumar lafiya ta kasar Sin, don kaddamar da jerin tarukan musayar dabarun dakile cutar COVID-19 ta kafar bidiyo, tsakanin kwararrun kasar Sin da takwarorinsu na kasashen Afirka.

A cewar mista Geng, a yau Litinin ne, aka fara yin taro na farko, inda jami'an lafiya na kasar Sin, da jami'an gwamnatoci da kwararrun ma'aikatan lafiya na kasashen Afirka sun yi musayar ra'ayoyi, kan fannonin dabarun kandagarkin annoba, da fasahohin kula da majiyyata, da dabarun gwaje-gwajen cututtuka, da dai makamantansu.

Jami'in na kasar Sin ya kara da cewa, kasar Sin za ta samar da karin kayayyakin kandagarkin cuta ga kasashen Afirka, gami da aike musu da karin tawagogin kwararrun jami'an lafiya, don tabbatar da samun nasarar kawar da cutar daga doron kasa baki daya. (Bello Wang)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China