Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Ministocin lafiyar G20: matakan da aka dauka bisa fasahar sadarwar zamani suna da muhimmanci wajen yaki da cutar COVID-19
2020-04-20 13:12:48        cri

Ministocin lafiyar kungiyar G20 sun bayyana a jiya Lahadi cewa, ya kamata a karfafa kwarewar kasa da kasa wajen yin kandagarki kan cututtuka masu yaduwa, sun kuma jaddada muhimmancin daukar wasu matakan da za a aiwatar da su bisa fasahar sadarwar zamani wajen warware matsalolin yaduwar cututtukan.

A wannan rana, kasar Saudiyya, dake shugabantar kungiyar a wannan karo, ta jagoranci gudanar da taron ministocin lafiyar na kasashe mambobin kungiyar G20 ta kafar bidiyo, jami'an da suka halarci taron sun yi musayar ra'ayoyi kan fasahohin yaki da cutar numfashi ta COVID-19, da kuma matakan da suka dauka domin dakile yaduwar annobar.

A yayin taron, ministocin sun fidda wata sanarwa cewa, dukkanin manufofi da matakan sun fidda su ne domin kiyaye lafiyar al'umma da kuma ba da tallafi gare su, da yaki da cutar, kana da karfafa ayyukan kiwon lafiyar kasa da kasa da kuma rage hasarar da wannan annoba za ta yiwa tattalin arzikin duniya.

Haka kuma, an ce, ministocin lafiyar kasashen G20 za su dauki karin matakai don hana yaduwar cutar COVID-19, kuma za su sake kiran wani taro a nan gaba idan bukatar hakan ta taso. (Maryam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China