Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
An bukaci al'ummar Afrika ta Kudu kada su tada hankalinsu sakamakon bullar cutar COVID-19 na farko a kasar
2020-03-06 10:24:17        cri
Majalisar dokokin kasar Afrika ta kudu, ta ce bai kamata al'ummar kasar su shiga fargaba ba, sakamakon tabbatar da bullar cutar numfashi ta COVID-19, karon farko a kasar.

Wannan na zuwa ne bayan Ministan lafiya na kasar Zweli Mkhize, ya bayyana samun mutum na farko da ya kamu da cutar a kasar.

Ministan ya bayyana a jiya cewa, cibiyar dakile cututtuka masu yaduwa ta kasar, ta ce sakamakon gwajin da aka yi wa wani da ake zaton na dauke da cutar, ya tabbtar ya kamu da ita, lamarin da ya sa kasar kara taka tsantsa.

Zweli Mkhize, ya ce mara lafiyan mai shekaru 38, ya je kasar Italiya tare da matarsa. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China