2020-03-03 12:27:25 cri |
Sanarwar ta ce hukumomin biyu a shirye suke su yi aiki tare da cibiyoyin kasa da kasa, da hukumomin kasashen duniya, musamman wajen ba da fifiko ga kasashen duniya masu karancin wadata wadanda tsarin kiwon lafiyarsu ba shi da inganci, kana mutanen kasashen ba su da galihu.
A cewar sanarwar, cibiyoyin biyu za su yi iyakar kokarinsu gwargwadon hali, wajen taimakawa kasashen ta bangarori daban daban da suka hada da, samar da kudaden ayyukan gaggawa, da bayar da shawarwari, da tallafin kwararru. Musamman wajen samar da kudaden da ake bukata cikin gaggawa, don taimakawa kasashen wajen tinkarar matsalolin idan bukatar hakan ta taso. (Ahmad Fagam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China