Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kasashen Syria da Libya sun amince su farfado da dangantakar diflomasiyya a tsakaninsu
2020-03-02 10:24:30        cri
Gwamnatin Syria da tawagar jami'an diflomasiyyar Libya dake ziyara a kasar, sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna, dongane da farfado da dangantakar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu.

Kamfanin dillancin labarai na SANA, ya ce an rattaba hannu kan yarjejeniyar ne biyo bayan taro da aka yi tsakanin Ministan harkokin wajen Syria, Walid al-Moallem da tawagar jami'an diflomasiyyar Libya, karkashin mataimakin Firaministan kasar Abdul-Rahman al-Ahiresh da ministocin harkokin wajen kasar Abdul-Hadi al-Hawaij.

Mambobin tawagar Libyar sun kuma jaddada kudurinsu na tunkarar tasirin kasashen waje.

Cikin sanawar da aka fitar ga manema labarai bayan taron, Ministan harkokin wajen Syria Walid al-Moallem, ya ce za a dawo da harkokin diflomasiyya na wucin gadi a biranen Damascus da Benghazi, har zuwa lokacin da za a bude ofishin Jakadancin kasar a Tripoli, nan bada dadewa ba.

A nasa bangaren, ministan harkokin wajen Libya Abdul-Hadi al-Hawaij, ya jaddada muhimmancin dawo da dangantakar diflomasiyya da tattalin arziki tsakanin kasashen biyu. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China