2020-02-11 20:23:19 cri |
A cewar hukumar kare hakkin bil Adama ta kasar, sojojin gwamnatin sun shafe tsawon makwanni, suna gwabza fada da 'yan tawaye, kafin cimma wannan nasara. Hakan ya kuma biyo bayan musayar wuta ta tsawon lokaci da suka yi a lardunan Idlib da Aleppo, wanda hakan ya ba su damar kwace zirin dake kunshe da babbar hanyar mota ta Idlib da kudancin Aleppo.
Wannan babbar hanya dai ta hada Aleppo, wanda shi ne babban yankin tattalin arzikin kasar ta Syria, da birnin Damascus fadar mulkin kasar, da kuma sauran sassan kudancin kasar. (Saminu)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China