2019-11-15 13:06:56 cri |
Kamfanin dillancin labarai na SANA, ya ruwaito Shugaban Syria Bashar al-Assad a jiya na cewa, fafutukar yaki da son zuciya na yammacin duniya na ci gaba da gudana.
Bashar al-Assad ya bayyana haka ne yayin ganawarsa da Mojtaba Zonnouri, shugaban hukumar kula da tsaro da harkokin kasa da kasa nan a Iran, wanda ya kai ziyara birnin Damascus a ranar Alhamis.
Shugaban na Syria ya jaddada cewa kasar za ta ci gaba da yaki da zalamar kasashen yamma ta hanyar farwa mayaka da jami'ansu, wadanda ake cin nasara kansu a wurare daban daban.
A nasa bangaren, Zonnouri ya ce Syria za ta yi nasara duk da wahalhalun da take fuskanta.
Tsawon lokacin da aka shafe ana yaki a Syria, Iran ce ta kasance babbar kawar gwamnatin Assad. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China